Wakilin sashin Hausa ya ce yanzu haka Ζ΄an unguwar na can suna ΖoΖarin kashe wannan Wuta da saurayin ya cinnawa gidan su budurwar tasa saboda an Ιaura aurenta da wani ma'aikacin kamfanin mai na Ζasa NNPC a Ιazu da misalin Ζarfe 2:00 na rana
Tun farko an bayyana cewar saurayin ya shafe kimanin shekaru 13 yana Ιawainiya da yarinyar tun shekara ta 2014 ya kammala karatun NCE yana jiran ya samu aikin yi bai samu ba sai a watan daya gabata ya tafi neman kuΙi jihar Legas bayan ya dawo a daren jiya sai ya samu labarin cewa
Za'a Ιaura auren budurwar sa da wani ma'aikacin NNPC wanda suka haΙu da budurwar Ζasa da mako guda inda ya ce shi zai Ιauki nauyin komai, yanzu haka dai an Ιaura auren, kunji fa kuna ganin iyayen budurwar sun yi masa adalci kuwa?


0 Comments